Posts

Showing posts from September, 2019

Karanta Martanin Hadiza Gabon Da Wani Yace Yanason Ya Mallaki Kamarta Ukku

Image
Wani ma'abocin shafin Twitter ya bayyana cewa idan aka yi nasarar samar da fasahar samar da kwafin mutum to shi zai sa a kawomai kalar Hadiza Gabon guda 3, daya da safe daya da rana daya da dare, wannan rubutu da yayi ya dauki hankula ta yanda har itama Hadizar ta mayar da martani. Hadizar ta ce mai Anya ba zai maka yawa ba?

Wani Mutum Ya daure yarsa Cikin gida Tsahon shekara 3 akan auren Dole

Image
Cikin Bidiyo Daga Nasir Salisu Zango GASKIYA ANA RASHIN IMANI: Ku kalli wannan bidiyon Allah ka takaita mana masifun Zamani, jiya muka Sami labarin wasu sun kona mutum da matarsa Mai tsohon ciki da yarsa Mai shekara .2 Yau kuma muka Gano wani mutum wanda ya daure 'ya'yansa biyu a gida tsahon shekaru 3 saboda sun yi masa wani laifi, har takai namjin ya mutu, a zuwa gaisuwa ne muka Gano macen kuma tuni an kubutar da ita shikuma mahaifinsu da matar sa suna hannun hukuma(yau zamu yi cikakken bayani a cikin shirye shiryen mu) to Amma Wai meke kawo ta azarar irin wadannan matsaloli ne? A kwanakin baya wani ya shiga har gida ya yanka Abokin kasuwancinsa, saboda yana son cinye masa naira miliyan 3 da yake binsa bashi, Dan haka ya Kira shi cewar zaizo gida ya kawo masa kudin, Amma kasancenwar yasan cewar mutumin ya Sami sabani da matarsa, sai yayi amfani da damar ya Debo Yan ta adda suka yanka mutumin suka kuma rubuta cewar, Wai shine ya kashe kansa saboda Rikicin sa da matar sa, Amma d

Wani Malami Ya Harsala Adam A Zango, Karanta Murtaninsa Akan Malamin

Image
Fitaccen jarumin nan na fina-finan Hausa Adam A. Zango ya karyata wani ‘malami’ da ya yi ikirarin cewa jarumin yana neman mata ‘yan kasa da shekara 20 da zummar tantance su domin ya sanya su a wani sabon fim dinsa. Malamin, wanda aka nuno shi a wani bidiyo yana huduba, ya ce jarumin ya fice daga masana’antar Kannywood ne saboda ba ya so hukumomi su tace fina-finansa da niyyar bin tsarin “tarbiyyar addinin musulunci”. Ya ce jarumin yana neman mata ‘yan kasa da shekara 20 domin ya sanya su a fim da zummar lalata tarbiyarsu da kuma hana hukumomin tace fina-finai yin aikinsu. Binciken da BBC ta yi dai ya nuna cewa jarumin ya fita daga Kannywood ne saboda “musgunawar da yake zargin ana yi wa ‘yan fim da mawaka a jihar Kano” inda hukumar tace fina-finan jihar ta kama wasu daga cikin su kwanakin baya. A bidiyon da Adam Zango ya wallafa domin martani ga malamin, jarumin ya dauki Alkur’ani mai tsarki, ya zargi malamin da “yin karya a kan abin da bai sani ba.” “Na rantse da Allah duk abin da [ma

Soyayya Ruwan zuma: Ty Shaba Ya Taya Tsohuwar matarsa zagayowar ranar haihuwarta Samira Ahmad (karanta Martanin Mutane)

Image
Soyayya ruwan zuma an rabu an dawo ana son juna ya kamata shi mijin da ita suyi hakuri ta dawo gidanta. Ga Posting dinsa a shafinsa na sada zumunta instagram.

Wata Sabuwa ! Sadiya Haruna Mai Kayan Mata, Daga Yau Matata ce Duk Abinda Zakuyi Kuyi - Jarumi Isah A Isah

Image
Shafin Legit ya kawo rahoto Jarumi Isa A. Isa yayi wata babbar magana a wani sabon bidiyo da ya wallafa - Inda ya bayyanawa mutane masu yawan tambayarsa dangantakar dake tsakaninsa da Sadiya Haruna - Jarumin ya bayyana cewa daga yau kowa ya sani cewa Sadiya Haruna matarsa ce Wani bidiyo da jarumin fina-finan Hausa na masana’antar Kannywood yayi ya bayyana dangantakar dake tsakaninsa da Sadiya Haruna, buurwar da ta ware waken bayar da shawarwari akan zaman aure da yadda mace zata rike miji ba tare da samun matsala ba. Jarumin dai ya bayyana cewa ana yawan tambayarshi dangantakar dake tsakanin shi da Sadiya Haruna, to yaş shine yayi alkawarin bayyanawa, ga abinde jarumin ya ce: “ Assalamu Alaikum Warahamatullahi Ta’ala Wabarakatuhum, jama’a kowa ya taso sai ya fara tambayata Isa wai yaya dangantakarshi tsakanin shi da Sadiya, kowa ba shi da aiki sai wannan, saboda haka daga yau ita matata, nagode.” Ana yawan ganin jarumin da Sadiya Haruna suna yawo tare ko kuma suna daukar hoto ko bidiyo

VIDEO : Kalli Mustapha Nabraska Yayi Magana Mai Muhimmaci Akan Abinda Yan Kwankwasiyya Nayiwa Dr Pantami

Image
Wanna magana tana da muhimmanci sosai wanda shine kwankwasiyya amana wanda mai Arewarmu Tv yayi kokarin dorawa a shafinsa na Youtube. Ga bidiyon nan kasa.

Tashin Hankali Guda Biyar Da Baza A Taba mantawa Basu Ba Har Abada a masana'antar Kannywood

Image
Abubuwa da dama sun faru tun bayan kafuwar masana'antar fina-finai ta Kannywood fiye da shekaru ashirin da suka gabata  - Sai dai akwai fitattun abubuwa da suka fi janyo kace-nace musamman a 'yan shekarun baya-bayan nan Legit ta ruwaito. Mun yi nazari akan abubuwa guda biyar da suka fi tayar da kura a masana'antar wacce ke da farin jini sosai. Hausaloaded ta sankamomu.  1. Abu na farko shine maganar auren jinsi Abinda ya ja hankali sosai kuma ya tada jijiyar wuya shine maganar hada auren jinsi da aka yiwa wasu taurarin Kannywood hudu da yin dabi'ar a watan Afrilun shekarar 2007, lamarin da ya saka suka shiga wasan buya da hukumar Hisba, bayan ta samu labarin sannan ta shiga nemansu.  Ko da yake a wata hira da ta yi da jaridar BBC, Aunty Maiduguri wacce aka zarga da hada auren ta musanta zargin.  2. Sai kuma abu na biyuwato gagarumar matsala da ita ma baza a manta da ita ba a wannan masana'antar ta Kannywood wato maganar fina-finan batsa. 'Yan Kannywood sun sa