Posts

Showing posts with the label Siyasa

Gudun muwa - Ibrahim Maishinku ya bugawa Shugaba Buhari fasta

Image
Tauraron fina-finan Hausa, Ibrahim Maishinku ya bugawa shugaban kasa, Muhammadu Buhari fastar yakin neman zabe inda ya bayyana goyon bayanshi gareshi a zaben shekarar 2019 me zuwa. Allah karamana zaman lapiya da kwanciyar Hankali a cikin wannan kasa tamu mai Albarka

Gudun muwa - Ibrahim Maishinku ya bugawa Shugaba Buhari fasta

Image
Tauraron fina-finan Hausa, Ibrahim Maishinku ya bugawa shugaban kasa, Muhammadu Buhari fastar yakin neman zabe inda ya bayyana goyon bayanshi gareshi a zaben shekarar 2019 me zuwa. Allah karamana zaman lapiya da kwanciyar Hankali a cikin wannan kasa tamu mai Albarka

Barayi sun daura damarar komawa kan mulkin Nigeria — APC

Image
Jam'iyyar APC mai mulkin Najeriya ta yi zargin cewa barayin da suka sace kudin kasar sun sake daura damarar komawa kan mulki bayan sun sha kaye a zabukan da suka gabata. Wata sanarwa da mai rokin mukamin kakakin jam'iyyar Mr. Yekini Nabena ya fitar anar Lahadi ta ce babu abin da barayin ke son yi illa sake kassara Najeriya. "Muna jawo hankalin 'yan Najeriya bisa shirin da wasu 'yan siyasa ke yi na sayen kuri'u da kuma yin amfani da su ta hanyar da bata dace ba da zummar tauye hakkin masu kada kuri'a a zabukan da ke tafe," in ji sanarwar. Sai dai Mr. Nabena bai bayar da wata hujja da ta nuna gaskiyar ikirarin da ya yi ba. A cewar sa, "mutanen su ne suka wawure kudaden jama'a domin gudanar da harkokin siyasarsu kamar yadda ya gabata a gwamnatocin da suka gabata, don haka dole a hana su kwata hakan a zabuka masu zuwa." Mai magana da yawun jam'iyyar APCn ya ce a cikin shekara uku gwamnatin Shugaba Muhammadu Buhari ta tsallake duk wasu ...

Barayi sun daura damarar komawa kan mulkin Nigeria — APC

Image
Jam'iyyar APC mai mulkin Najeriya ta yi zargin cewa barayin da suka sace kudin kasar sun sake daura damarar komawa kan mulki bayan sun sha kaye a zabukan da suka gabata. Wata sanarwa da mai rokin mukamin kakakin jam'iyyar Mr. Yekini Nabena ya fitar anar Lahadi ta ce babu abin da barayin ke son yi illa sake kassara Najeriya. "Muna jawo hankalin 'yan Najeriya bisa shirin da wasu 'yan siyasa ke yi na sayen kuri'u da kuma yin amfani da su ta hanyar da bata dace ba da zummar tauye hakkin masu kada kuri'a a zabukan da ke tafe," in ji sanarwar. Sai dai Mr. Nabena bai bayar da wata hujja da ta nuna gaskiyar ikirarin da ya yi ba. A cewar sa, "mutanen su ne suka wawure kudaden jama'a domin gudanar da harkokin siyasarsu kamar yadda ya gabata a gwamnatocin da suka gabata, don haka dole a hana su kwata hakan a zabuka masu zuwa." Mai magana da yawun jam'iyyar APCn ya ce a cikin shekara uku gwamnatin Shugaba Muhammadu Buhari ta tsallake duk wasu ...

Ganduje ya yi bankwana da jar hula

Image
Gwamnan Kano Abdullahi Umar Ganduje ya yi watsi da jar hula a yayin da tsohon gwamnan jihar Malam Ibrahim Shekarau ya kai masa ziyara ranar Asabar, jim kadan bayan ya bayyana cewa ya koma jam'iyyar APC mai mulkin Najeriya. Sanya jar hula alama ce ta yin biyayya ga sanata Rabi'u Kwankwaso, mutumin da suka raba gari da Gwamna Ganduje bayan sun yi shekara da shekaru suna harokokin siyasa tare. Malam Shekarau, wanda ya ziyarci Gwamna Ganduje sanye da bakaken tufafi, ya taras da Gwamna Ganduje sanye da nasa bakaken tufafin, ciki har da bakar hula - ba ja ba - kamar yadda ya saba. Ya ce ya fice daga jam'iyyar PDP mai hamayya ce saboda rashin adalcin da aka yi masa. Gabanin fitar sa daga PDP, tsohon gwamnan ya nuna rashin jin dadinsa kan matakin da PDP ta dauka na rusa shugabancin jam'iyyar na jihar Kano, kana aka maye gurbin sa da kwamotin rikon-kwarya mai mambobi bakwai. A cikin mambobin, biyu ne kawai 'yan bangaren Malam Shekarau, yayin da biyar ke bangaren tsohon gwam...

Ganduje ya yi bankwana da jar hula

Image
Gwamnan Kano Abdullahi Umar Ganduje ya yi watsi da jar hula a yayin da tsohon gwamnan jihar Malam Ibrahim Shekarau ya kai masa ziyara ranar Asabar, jim kadan bayan ya bayyana cewa ya koma jam'iyyar APC mai mulkin Najeriya. Sanya jar hula alama ce ta yin biyayya ga sanata Rabi'u Kwankwaso, mutumin da suka raba gari da Gwamna Ganduje bayan sun yi shekara da shekaru suna harokokin siyasa tare. Malam Shekarau, wanda ya ziyarci Gwamna Ganduje sanye da bakaken tufafi, ya taras da Gwamna Ganduje sanye da nasa bakaken tufafin, ciki har da bakar hula - ba ja ba - kamar yadda ya saba. Ya ce ya fice daga jam'iyyar PDP mai hamayya ce saboda rashin adalcin da aka yi masa. Gabanin fitar sa daga PDP, tsohon gwamnan ya nuna rashin jin dadinsa kan matakin da PDP ta dauka na rusa shugabancin jam'iyyar na jihar Kano, kana aka maye gurbin sa da kwamotin rikon-kwarya mai mambobi bakwai. A cikin mambobin, biyu ne kawai 'yan bangaren Malam Shekarau, yayin da biyar ke bangaren tsohon gwam...

Halin da na samu Sambo Dasuki tsare a hannun DSS -Jones Abiri

Image
Cikin wata tattaunawa ta musamman da PREMIUM TIMES ta yi da dan jaridar nan da ya shafe shekaru biyu a tsare a hannun SSS da a yanzu aka fi sani da DSS, bayan ya fito, Jones Abiri ya bayyana irin zaman kuncin da ya yi a tsare, kuma ya bada labarin irin halin da ya samu tsohon mai bada shawara a kan harkokin tsaro, na lokacin Goodluck Jonathan, Sambo Dasuki ke ciki. PT: Ko ka samu yin katarin ganin Sambo Dasuki a inda SSS suka tsare ka a Abuja kuwa? ABIRI: Tabbas na hadu da Sambo Dasuki amma fa ba a daki daya aka tsare mu ni da shi ba. Kun san su ai manya ne. Amma fa duk da haka ina tabbatar muku da cewa a inda ya ke a tsare yanzu ko wurin bayan gida babu. A duk lokacin da ya matsu, sai dai su fito da shi su kai shi wani wuri can daban. To ta wannan dalili ne har mu ke iya ganin sa idan an fito da shi zai dan zagaya ban-daki. Amma akwai ma lokacin da mu ka hadu gaba da gaba, har ma na mika masa hannu muka gaisa. A lokacin ya fito ne zai je ban daki, ni kuma ina tsaye a wajen dakin mu....

Halin da na samu Sambo Dasuki tsare a hannun DSS -Jones Abiri

Image
Cikin wata tattaunawa ta musamman da PREMIUM TIMES ta yi da dan jaridar nan da ya shafe shekaru biyu a tsare a hannun SSS da a yanzu aka fi sani da DSS, bayan ya fito, Jones Abiri ya bayyana irin zaman kuncin da ya yi a tsare, kuma ya bada labarin irin halin da ya samu tsohon mai bada shawara a kan harkokin tsaro, na lokacin Goodluck Jonathan, Sambo Dasuki ke ciki. PT: Ko ka samu yin katarin ganin Sambo Dasuki a inda SSS suka tsare ka a Abuja kuwa? ABIRI: Tabbas na hadu da Sambo Dasuki amma fa ba a daki daya aka tsare mu ni da shi ba. Kun san su ai manya ne. Amma fa duk da haka ina tabbatar muku da cewa a inda ya ke a tsare yanzu ko wurin bayan gida babu. A duk lokacin da ya matsu, sai dai su fito da shi su kai shi wani wuri can daban. To ta wannan dalili ne har mu ke iya ganin sa idan an fito da shi zai dan zagaya ban-daki. Amma akwai ma lokacin da mu ka hadu gaba da gaba, har ma na mika masa hannu muka gaisa. A lokacin ya fito ne zai je ban daki, ni kuma ina tsaye a wajen dakin mu....

Dalilin da ya sa arewacin Nigeria ya fi kudanci fama da talauci

Image
Wani masanin tattalin arziki ya ce arewacin Najeriya ya fi kudancin kasar fama da matsanancin talauci ne saboda ba ya sa samun kudin shigar da ya kai na kudu. Dr Zahumnam Dapel ya shaida wa BBC cewa "kudaden shigar da jihohin Lagos da Ribas suke samu a shekara sun fi wadanda jihohi 14 na arewacin kasar ke samu, don haka suna da damar da za su kashe su kan al'umominsu." Masanin tattalin arzikin, wanda ya yi aiki a Amurka, ya kara da cewa yawan talakawa da ke ci gaba da haihuwa ba tare da samun abin da za su bai wa iyalansu ba a arewacin Najeriya ya taimaka wajen ta'azzara talaucin da yankin ke ciki. A cewar sa, jami'o'in da ke kudancin kasar sun fi na arewacin kasar, yana mai cewa "daga shekarar 1989 jami'oi 12 ne a arewa yayin da kudu ke da 17, amma a 2017 akwai jami'o'i 58 a arewa yayin da kudanci ke da 102. Idan kana ba mutum ilimi za ka fitar da shi daga talauci." Ya kara da cewa satar da wasu 'yan siyasa ke yi ta kara jefa arewac...

Dalilin da ya sa arewacin Nigeria ya fi kudanci fama da talauci

Image
Wani masanin tattalin arziki ya ce arewacin Najeriya ya fi kudancin kasar fama da matsanancin talauci ne saboda ba ya sa samun kudin shigar da ya kai na kudu. Dr Zahumnam Dapel ya shaida wa BBC cewa "kudaden shigar da jihohin Lagos da Ribas suke samu a shekara sun fi wadanda jihohi 14 na arewacin kasar ke samu, don haka suna da damar da za su kashe su kan al'umominsu." Masanin tattalin arzikin, wanda ya yi aiki a Amurka, ya kara da cewa yawan talakawa da ke ci gaba da haihuwa ba tare da samun abin da za su bai wa iyalansu ba a arewacin Najeriya ya taimaka wajen ta'azzara talaucin da yankin ke ciki. A cewar sa, jami'o'in da ke kudancin kasar sun fi na arewacin kasar, yana mai cewa "daga shekarar 1989 jami'oi 12 ne a arewa yayin da kudu ke da 17, amma a 2017 akwai jami'o'i 58 a arewa yayin da kudanci ke da 102. Idan kana ba mutum ilimi za ka fitar da shi daga talauci." Ya kara da cewa satar da wasu 'yan siyasa ke yi ta kara jefa arewac...

ZAN INGANTA NOMAN WIWI A NAJERIYA IDAN NA ZAMA SHUGABAN KASA

Image
Zan inganta noman Wiwi a Nigeria ta yadda zamu kasance kasar data fi kowacce kasa a duniya noman Tabar wiwi. Omoyele Sowore dan takarar kujerar shugaban Nigeria shine ya bayyana haka, har yake cewa tabar wiwin da ake nomawa yanzu haka a jihar Ekiti itace mafi inganci da bugarwa a dukkan duniya. Noman wiwi tare da fitar da ita kasashen waje zai samar da kudaden shiga sama da fetur, don haka idan na zama shugaban Nigeria zan tabbata ana nomata a dukkan jihohin Nigeria. Daga Rabiu Biyora Source:- Hutudole

ZAN INGANTA NOMAN WIWI A NAJERIYA IDAN NA ZAMA SHUGABAN KASA

Image
Zan inganta noman Wiwi a Nigeria ta yadda zamu kasance kasar data fi kowacce kasa a duniya noman Tabar wiwi. Omoyele Sowore dan takarar kujerar shugaban Nigeria shine ya bayyana haka, har yake cewa tabar wiwin da ake nomawa yanzu haka a jihar Ekiti itace mafi inganci da bugarwa a dukkan duniya. Noman wiwi tare da fitar da ita kasashen waje zai samar da kudaden shiga sama da fetur, don haka idan na zama shugaban Nigeria zan tabbata ana nomata a dukkan jihohin Nigeria. Daga Rabiu Biyora Source:- Hutudole

Canja jam’iyya ba tsere wa EFCC ba ne – Magu

Image
Shugaban Riko na Hukumar EFCC, Ibrahim Magu, ya bayyana cewa ‘yan siyasa da ke ficewa daga wannan jam’iyya zuwa waccan, ba alamomi ba ne da ke nuna cewa sun tsere wa EFCC daga gurfanar da duk wani cikin su wanda ya wawuri dukiyar gwamnati. Da ya ke jawabi a wurin wata ganawar musamman da ya yi da editocin wasu jaridun kasar nan a Lagos, Magu ya ce babu wurin buya ga irin wadannan ‘yan siyasa, ballantana su fake daga kamu da, bincike da kuma gurfanarwar da EFCC za ta yi musu. “Kotu ce kawai za ta iya wanke mutun daga zargin ko ya ci kudi ko bai ci ba. Idan ya ci za ta hukunta shi, idan bai ci kudi ba kuwa, za ta sallame shi.” Da ya ke maida martani daga wata tambaya da aka yi masa cewa jam’iyyar APC mai mulki na yin katsalandan a cikin aikin EFCC, Magu cewa ya yi, bai taba samun wani umarni ko koron yin wata alfarma kan wani bincike ya hukumar sa ke yi ba. Magu cewa ya yi abin ya zama tamkar al’ada ga ‘yan siyasa idan ana binciken su sai su rika cewa ana yi musu bi-ta-da-kulli na siyas...

Canja jam’iyya ba tsere wa EFCC ba ne – Magu

Image
Shugaban Riko na Hukumar EFCC, Ibrahim Magu, ya bayyana cewa ‘yan siyasa da ke ficewa daga wannan jam’iyya zuwa waccan, ba alamomi ba ne da ke nuna cewa sun tsere wa EFCC daga gurfanar da duk wani cikin su wanda ya wawuri dukiyar gwamnati. Da ya ke jawabi a wurin wata ganawar musamman da ya yi da editocin wasu jaridun kasar nan a Lagos, Magu ya ce babu wurin buya ga irin wadannan ‘yan siyasa, ballantana su fake daga kamu da, bincike da kuma gurfanarwar da EFCC za ta yi musu. “Kotu ce kawai za ta iya wanke mutun daga zargin ko ya ci kudi ko bai ci ba. Idan ya ci za ta hukunta shi, idan bai ci kudi ba kuwa, za ta sallame shi.” Da ya ke maida martani daga wata tambaya da aka yi masa cewa jam’iyyar APC mai mulki na yin katsalandan a cikin aikin EFCC, Magu cewa ya yi, bai taba samun wani umarni ko koron yin wata alfarma kan wani bincike ya hukumar sa ke yi ba. Magu cewa ya yi abin ya zama tamkar al’ada ga ‘yan siyasa idan ana binciken su sai su rika cewa ana yi musu bi-ta-da-kulli na siyas...

Su wa suka saya wa Buhari fom din takara?

Image
Wasu matasan Najeriya sun saya wa shugaban kasar Muhmmadu Buhari fom din takara a kan Naira miliyan 45. Matasan na kungiyar Nigeria Ambassadors Consolidation Network sun saya wa shugaban fom din ne jim kadan bayan jam'iyyar APC mai mulkin kasar ta fitar da kudaden da masu neman takara a jam'iyyar za su sayi fom. Fom din shugaban kasa ne ya fi kowanne tsada, da ake sayar da shi a kan Naira miliyan 45. To sai dai abin da mutane da dama ke mamaki shi ne yadda matasan suka sami miliyoyin kudin da suka saya wa Buhari fom din. Bugu da kari hakan ya faru ne a daidai lokacin da wasu 'yan uwansu matasa ke korafin cewa kudin da jam'iyyar ta sanya ya yi musu tsada. Akwai masu ra'ayin cewa matasan na rawa ne da bazar wasu manyan 'yan siyasa da suka ba su kudin sayen fom din, don a nuna cewa har yanzu Buhari yana da farin jini a wajen matasan kasar. To sai dai shugaban kungiyar ta Nigeria Ambassadors Consolidation Network Barista Sanusi Musa ya ce ko kadan ba bu wani jami...

Su wa suka saya wa Buhari fom din takara?

Image
Wasu matasan Najeriya sun saya wa shugaban kasar Muhmmadu Buhari fom din takara a kan Naira miliyan 45. Matasan na kungiyar Nigeria Ambassadors Consolidation Network sun saya wa shugaban fom din ne jim kadan bayan jam'iyyar APC mai mulkin kasar ta fitar da kudaden da masu neman takara a jam'iyyar za su sayi fom. Fom din shugaban kasa ne ya fi kowanne tsada, da ake sayar da shi a kan Naira miliyan 45. To sai dai abin da mutane da dama ke mamaki shi ne yadda matasan suka sami miliyoyin kudin da suka saya wa Buhari fom din. Bugu da kari hakan ya faru ne a daidai lokacin da wasu 'yan uwansu matasa ke korafin cewa kudin da jam'iyyar ta sanya ya yi musu tsada. Akwai masu ra'ayin cewa matasan na rawa ne da bazar wasu manyan 'yan siyasa da suka ba su kudin sayen fom din, don a nuna cewa har yanzu Buhari yana da farin jini a wajen matasan kasar. To sai dai shugaban kungiyar ta Nigeria Ambassadors Consolidation Network Barista Sanusi Musa ya ce ko kadan ba bu wani jami...

Sabuwa Wakar Rarara - Kowa Ya Fito Barawo ne (Indai Manufar A Gyara ne)

Image
Rarara Ya chachaki wani mawakin PDP dan Baki Wannan wata sabuwa waka ce wanda rara yayi domin kuwa idan zaku tuna a baya yayi waka mai taken "kowa ya fita shi barawo ne" to yau yayi sabuwa mai suna "kowa ya fito barawo ne ,indai manufar barawo ne" wanda gaskia wakar tayi dadi sosai. Ma'ana duk wanda ya fito takara da shi to barawo ne. Download Here Share pls

Sabuwa Wakar Rarara - Kowa Ya Fito Barawo ne (Indai Manufar A Gyara ne)

Image
Rarara Ya chachaki wani mawakin PDP dan Baki Wannan wata sabuwa waka ce wanda rara yayi domin kuwa idan zaku tuna a baya yayi waka mai taken "kowa ya fita shi barawo ne" to yau yayi sabuwa mai suna "kowa ya fito barawo ne ,indai manufar barawo ne" wanda gaskia wakar tayi dadi sosai. Ma'ana duk wanda ya fito takara da shi to barawo ne. Download Here Share pls

Tsohon gwamnan Kano Ibrahim Shekarau ya fice daga PDP

Image
Tsohon gwamnan Kano Malam Ibrahim Shekaru ya fice daga jam'iyyar PDP. Da asubahin Talatar nan ne Shekarau ya bayyana ficewa daga PDP, a cewar mai magana da yawunsa Malam Sule Ya'u Sule. Shekarau, wanda yana daya daga masu neman takarar shugabancin Najeriya a jami'iyyar PDP ya ce ya fice ne daga jam'iyyar saboda zargin rashin adalci a bangaren shugabannin jam'iyyar na kasa, wajen rushe shugabancin jam'iyyar na jihar Kano, da yunkurin mikawa Kwankwaso shugabancin. A ranar Litinin ma wasu dubban yan PDP a Kano sun yi wata zanga-zangar nuna adawa da matakin uwar jam'iyyar. Shekarau ya ce gabanin daukar wannan mataki, sai da suka zauna da shugabancin PDP na kasa har sau hudu domin gabatar da korafinsu, da kuma kokari warware matsalar. Har yanzu ba a kai ga bayyana 'yan kwamitin ba, sai dai wasu kafofin yada labaran Najeriya sun ruwaito cewa makusantan Kwankwaso za a nada. A ranar Asabar din da ta gabata ne uwar jam'iyyar PDP ta kasa ta bayar da sanarwar...

Tsohon gwamnan Kano Ibrahim Shekarau ya fice daga PDP

Image
Tsohon gwamnan Kano Malam Ibrahim Shekaru ya fice daga jam'iyyar PDP. Da asubahin Talatar nan ne Shekarau ya bayyana ficewa daga PDP, a cewar mai magana da yawunsa Malam Sule Ya'u Sule. Shekarau, wanda yana daya daga masu neman takarar shugabancin Najeriya a jami'iyyar PDP ya ce ya fice ne daga jam'iyyar saboda zargin rashin adalci a bangaren shugabannin jam'iyyar na kasa, wajen rushe shugabancin jam'iyyar na jihar Kano, da yunkurin mikawa Kwankwaso shugabancin. A ranar Litinin ma wasu dubban yan PDP a Kano sun yi wata zanga-zangar nuna adawa da matakin uwar jam'iyyar. Shekarau ya ce gabanin daukar wannan mataki, sai da suka zauna da shugabancin PDP na kasa har sau hudu domin gabatar da korafinsu, da kuma kokari warware matsalar. Har yanzu ba a kai ga bayyana 'yan kwamitin ba, sai dai wasu kafofin yada labaran Najeriya sun ruwaito cewa makusantan Kwankwaso za a nada. A ranar Asabar din da ta gabata ne uwar jam'iyyar PDP ta kasa ta bayar da sanarwar...