Dalilin da ya sa nake damuwa da Nigeria – Bill Gates


Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Bill Gates, ya ce Najeriya tana daya daga cikin kasashen da yake sanya ido kansu sosai. Bill Gates wanda ya bayyana haka a wata hira da BBC, ya ce kasar tana da muhimmanci ne a wurinsa saboda ita ce ta fi kowace kasa yawan al'umma a nahiyar Afirka. "Wannan ne ya sa gidauniyarta ta Bill & Melinda Gates Foundation take ci gaba da aikace-aikacenta a can," kamar yadda ya ce. Har ila yau, ya ce akwai babban kalubale a fannin kiwon lafiya a yankin arewacin kasar. "Akwai matsalar cutar maleriya da kuma batun 'yan gudun hijira. Muna aiki da wadansu daga cikin gwamnatocin jihohi kamar na Kano da Borno a kokarinmu na ganin mun magance kalubalen kiwon lafiya a yankin," in ji shi.
Ya ce ayyukan gidauniyarsa suna taimakawa wajen rage mutuwar mata masu juna biyu da kuma kananan yara a fadin kasar. Sai dai ya ce suna aiki ne tare da gwamnatin kasar da kungiyoyi masu zaman kansa da kuma attajirin nan da ya fi kowa arziki a nahiyar Afirka, Alhaji Aliko Dangote - wanda dan kasar ne. Kamar sauran kasashen Afirka, Najeriya na daya daga cikin kasashen da aka fi yawan samun mace-macen mata wajen haihuwa da kuma na kananan yara.

Comments

Popular posts from this blog

BRIEF BIOGRAPHY OF SHEIKH IBRAHIM AHMAD MAQARY, IMAM OF NATIONAL MOSQUE ABUJA

Wane Ne Sheik Abul Fatahi Maiduguri? Karanta cikakken tarihin sa

TARIHI: ZUWAN TURAWA KASAR HAUSA DA YADDA SUKA CI KANO DA SOKOTO DA YAKI A SHEKARAR 1903.