TARIHI: ZUWAN TURAWA KASAR HAUSA DA YADDA SUKA CI KANO DA SOKOTO DA YAKI A SHEKARAR 1903.


TARIHI: ZUWAN TURAWA KASAR HAUSA DA YADDA SUKA CI KANO DA SOKOTO DA YAKI A SHEKARAR 1903. Kashi na Uku Daga Sadiq Tukur Gwarzo Can da Yammaci, sai suka aika manzonsu zuwa ga Mai unguwa Mallam Na-marwa, da cewar "Mu turawa da muka zo wannan birni ayau, muna son ka sanar da dukkan larabawa mazauna birnin nan naku cewa muna son su hallara a gabanmu manyansu da k'ananunsu har da bayinsu baki ɗaya suna masu biyayya ga umarnin mu". Ai kuwa koda mai unguwa ya labarta musu umarnin turawa, sai suka ce "munji kuma munyi biyayya." Nan take kuwa suka fara taruwa a kofar fadar kano. Da larabawan nan suka gama hallara, sai turawa suka fito a garesu, suka zauna reras akan kujeru suna fuskantar larabawan da suma suke a zaune. Shugaban turawa ya kira tafintansa wanda bamu san sunan saba, sannan yace ya tsaya a tsakiya domin soma aikinsa. Daga nan sai akace masa ya tambayi larabawan nan cewa iya su kaɗai kenan mazauna wannan birni? Tafinta ya sauya harshe gami da tambayar larabawa kamar yadda aka umarceshi. Take sai larabawa auka amsa da cewar "Iya mu kaɗai kenan, in banda matayenmu da kananun yara da muka bari a gida." Nan ma tafinta ya fassarawa turawa abinda suka faɗa. Sai kuma turawa suka kara cewa ku faɗawa waɗannan mutanen cewa "Yaku bak'i mazauna wannan kasa, babu damuwa da zata riske ku. Ba muzo domin kuba, ko kuma domin wanin kuba. Ba kuma kusan dalilin zuwan muba, ko kuna da masaniya game da haka?" Da larabawa suka ji haka sai suka amsa da cewa "Ya shugaba, mu fatake ne kurum waɗanda kaduwanci ya kawo mu wannan kasa don haka Ɓbamusan komai game da harkar (sarauta) gwamnati ba" Sai shugaban Turawa ya sake cewa "kuyi sani yaku larabawa, zuwan mu wannan kasa yana da sila da kuma dalili. Mu mutanen yammaci ne, kuma muna da wani ɗan uwa da ake kira Bature mai Launi. Shi ya kasance shugaban mune wanda ya zauna a wani gari mai suna 'Kafin-Yamusa'.. Ko kuna da masaniyar haka?" Sai larabawa suka amsa da cewar "kwarrai munji labarin haka". Sai shugaban turawa ya cigaba da cewar "Hakika, ɗanuwanmu yazo wannan kasa ya samu sarkin kasar Mai suna Magaji ɗan Yamusa wanda ya karɓeshi cikin girmamawa da kulawa tare da martabawa. Ya zauna tare dashi da alkawarin zasu taimaki junansu. Watarana, marigayi ɗanuwanmu yana zaune, shi bai san cewa magauta sun shiga tsakaninsu da magaji ɗan Yamusa ba, sai kurum Magaji ɗan Yamusa ya shigo gareshi tare dayi masa kisan gilla ba tare da ɗanuwanmu ya aikata masa wani kuskure ba. Bayan haka, sai Magaji ɗan yamusa ya rugo izuwa ga sarkin kano Ali alokacin da yaji muna nan tafe domin neman mafaka. Shikuma Sarkin kano Ali sai ya bashi mafaka tare da ɗaukaka darajarsa, har ya bashi muhalli mai kyau, da kuɗi, da bayi da dawakai na hawa. Munji wannan labari ne daga mutane dangane da abinda Sarki Ali ya yiwa wanda yayi mana laifi, kuma mun kamu da matsanancin ɓacin rai dangane da haka. Don haka muka zo nan da fatan mu kama Sarki Ali da abokinsa Magaji ɗan Yamusa. Gashi munzi kuma bamu tarar dasu ba". Shugaban Turawa yaci gaba da cewa " yaku larabawa ku sani cewar bani da labarin Sarki Ali yayi tafiya izuwa sokoto. Kuma ina rantsuwa gareku da cewar idan da mun san haka, kuma mun tabbatar da hakan, da babu abinda zai kawo mu wannan gari. Ina muku rantsuwa guda uku abisa haka (wallahi, Tallahi, Billahi kamar yadda yake a al'adar su larabawan wajen tabbatar da abu na gaskiya). Kuma Tabbas mun samu labarin sirri akan hanyarmu ta zowa nan cewar Sarki Ali ya tafi sokoto amma ban baiwa labarin amanna ba. Amma da ace na gamsu dashi, da sokoto na nufa ba nan ba. Munzo nan ne kurum ta dalilin Sarkin Ali da abokinsa Magaji, don haka ku kwantar da hankalinku a game damu. Kada kuji tsoro, tabbas ba zaku tozar taba, ba kuma zamu firgita kuba." Daga nan sai turawa suka sake cewa "A yanzu zamu tafi neman Inda Ali da Magaji suke. Idan kuna da saye da siyarwa kuna iya cigaba dayi da abokanan hurɗarku. Amma a tare damu da akwai hatsi da zamu so ku nik'a mana shi a matsayin abincin mu bisa son ranku ba bisa tilastawa ba". Larabawan nan suka ɗauka baki ɗayan su cewar "Munji kuma munyi biyayya da hakan, muna muku marhaban lale tare da duk abinda kuka zo dashi" Shikenan, abinda akayi kenan. Daga nan sai turawa suka fito da buhuna saba'in na hatsi, suka umarci masu yi musu dakon kaya su ɗauka subi larabawa dashi izuwa gidajensu. Sukuwa larabawa, sai suka rarraba hatsin ga iyalansu, suka umarcesu da su nika tsabar hatsin nan da gaggawa. Ai kuwa da yammacin wannan rana suka soma aikin, kuma gari baiyi duhu sosai ba suka kammala, a inda larabawan suka harhaɗa garin tare da aikawa ga turawa suna sanar nusu da cewa an kammala aiki. Kwana biyu bayan haka, sai turawa suka sake aikowa larabawa da buhunan hatsi guda dari biyu, suna masu neman a nika musu su. A wannan karon ma, iyalan larabawan sun kammala aikin a yini guda. Ai kuwa turawa sunyi matukar murna gami da farin ciki da hakan, sun kuma yi godiya sosai ga larabawan. Bayan haka, sai turawa suka yanke shawarar fita domin neman Sarkin Kano Ali da abokinsa Magaji ɗan Yamusa. Bayan sun gama shiri sai suka fita daga kano, amma sun bar wasunsu waɗanda zasu tsare gari. Su kuwa sai suka nufi sokoto. Akan hanyar sune sukayi kiciɓus da wasu dakarun Kano waɗanda suke dawowa daga sokoto (Ainihinsu tare suke da Sarki Ali, amma saboda yaji labarin turawa sai ya sulale ya barsu. Zakuji labarin su a gaba). Waziri Amadu ne ke jagorancin wannan tawaga, anyi wannan haɗuwa ne kuma a wani daji da ake kira 'Dajin Rubin' (Tana kuma iya yiwuwa turawa ne suka sanyawa dajin wannan suna saboda mutuwar ɗanuwansu Reuben a dajin) Da gamuwar su sai faɗa ya kaure a tsakani. Aka soma fafatawa, dakarun waziri Amadu suna afkawa turawa da sara da suka, yayin da suma turawa suka mayarwa da dakarun martani da harbi. Sai dai cikin abinda baifi awa ɗaya ba, turawa suka karya lagon wanna tawaga suka kuma watsa ta. Ya zamana an kashe wasu, wasu kuma suna zube a kakkarye harsashi yayi misu lahani, yayin da saura suka shige daji da gudu suna masu neman tsira da rayukansu..

Comments

Popular posts from this blog

Dadin kowa sabon salo episode 15

Dadin kowa sabon salo episode 15