Jam'iyyar PDP ta baiwa Ummi Zeezee babban mukami




Rahotanni sun kawo cewa babban jam’iyyar adawan Najeriya, PDP ta baiwa tsohuwar jarumar fina-finan Hausa na Kannywood, Ummi Zeezee babban mukami.

An bata mukamin shugabar riko ta mata ta kungiyar dake yiwa PDP kamfe gida-gida ta kasa baki daya.

Ummi da take bayyana hakan a shafinta na sada zumunta da muhawara tace ta godewa Allah da wannan mukami da ta samu yau, kuma tana fatan Allah ya baiwa jam'iyyar ta PDP mulki a zaben shekarar 2019.


Ummi dai tayi suna wajan caccakar gwamnatin shugaba Muhammadu Buhari.

Hakazalika shugaban kungiyar yiwa PDP kamfen gida-gida na kasa, Ibrahim Dahiru Danfulani ya tabbatar da wannan mukami na Ummi Zeezee a jiya Juma'a.

Naij hausa

Comments

Popular posts from this blog

BRIEF BIOGRAPHY OF SHEIKH IBRAHIM AHMAD MAQARY, IMAM OF NATIONAL MOSQUE ABUJA

Nafi Jin Dadin Sauraron Wakar Sauran Mawaka fiye Da Tawa - Inji Nura M Inuwa

Wane Ne Sheik Abul Fatahi Maiduguri? Karanta cikakken tarihin sa