Dandalin Kannywood: Ali Nuhu zai sake shirya Fim din Mujadala don tunawa da Ahmad S Nuhu




Zuwa yanzu a iya cewa shirye shirye sun nisa matuka game da sabunta shirin shahararren Fim din nan da yayi suna a shekarun baya, watau Mujadala, sai dai abinda ya ja hankali yan kallo shi ne wanda zai maye gurbin marigayi Ahmad S nuhu.

BBC Hausa ta ruwaito Kamfanin shirya Fina finai na Mai Shadda ne zai dauki nauyin shirya wannan Fim, inda tace a ranar 10 ga watan Mayu ne zata fara nadirsa, haka zalika kamfanin ta bayyana cewar jarumi Umar M Shareef ne zai maye gurbin Ahmad.


Shi dai wannan Fim ya shahara a tsakanin yan kallo da masu bibiyan fina finan Kannywood, wanda ya kunshi taurari kamarsu Ali Nuhu, Sani mai Iska, Fati Muhammad, Abida Muhammad, Maijidda Abdulkadir da kuma Ahmad S Nuhu, wanda shine ya fitaccen jarumi a Fim din.

Majiyar NAIJ.com ta ruwaito Ahmad ya rasu ne a shekarar 2007 sakamakon hadari da ya rutsa da shi a kan hanyarsa ta zuwa Maiduguri bayan fitowarsa daga garin Azare na jihar Bauchi inda ya gudanar da wasan Sallah.

A zamaninsa, Ahmad ya kasance jarumi mai tashe, domin kuwa tararuwarsa na haskawa, kuma yana da farin jinni a wajen yan kallo, gas hi mutum mai dadin hulda kamar yadda abokansa da na kusa suka tabbata

Comments

Popular posts from this blog

Dadin kowa sabon salo episode 15

Dadin kowa sabon salo episode 15