Dandalin kannywood: Rahma Sadau ta samu lambar yabo a matsayin jarumar jarumai na shekara



Rahotanni dake zuwa mana sun nuna cewa fitacciyar jarumar nan ta Kannywood, Rahama Sadau ta samu karramawa na musamman daga jaridar Leadership.

Ta samu lambar yabo a matsayin jarumar jarumai na wannan shekara. An kuma karramar jarumar ne a wajen bikin karrama fitattun yan Najeriya da suka kawo cigaba a kasar wanda aka gudanar a babban birnin tarayya Abuja.

An gudanar da bikin ne a daren ranar Alhamis, 24 ga watan Mayu.

Anyi bikin ne alhalin jarumar na kasar Cyprus saboda haka Uzee Usman ya wakilce ta.


Tayi ma dinbim masoyan ta godiya bisa goyon bayan da suke bata na yau da kullum wanda dashi take takama.

Daga karshe tayi ma jaridar Leadership godiya ta karramawar da suka bata tare da Uzee wanda ya amshi kyuatar a madadin ta.

Comments

Popular posts from this blog

BRIEF BIOGRAPHY OF SHEIKH IBRAHIM AHMAD MAQARY, IMAM OF NATIONAL MOSQUE ABUJA

Wane Ne Sheik Abul Fatahi Maiduguri? Karanta cikakken tarihin sa

TARIHI: ZUWAN TURAWA KASAR HAUSA DA YADDA SUKA CI KANO DA SOKOTO DA YAKI A SHEKARAR 1903.