Gwamnatin APC gwamnatin dabbobi ce -Inji Fayose




Gwamnan Jihar Ekiti mai barin gado, Ayo Fayose, ya bayyana gwamnatin APC da cewa gwamnati ce mai mulki tamkar na dabbobi.
Fayose ya yi wannan kakkausar furuci ne a lokacin da ya kai jaje ga Shugaban Majalisar Dattawa Bukola Saraki da Mataimakin sa Ike Ekweremadu bisa ga mamaya da shingen da jami’an tsaro suka yi musu a jiya Talata.
Da ya ke magana, Fayose wanda ya kai ziyarar a Majalisa, ya jinjina wa Sanatocin kasar nan bisa abin da ya kira jajircewar da suka yi wajen kare dimokradiyya daga masu yi mata hawan-kawara.
“Wannan ai mulkin dabbobi ne, domin dabba ita ce ke lalatawa ko ruguje abu. Ba ta da wani alfanu ga al’umma.
“Da a ce PDP ta yi irin wannan haukan a 2015, ai da su yanzu ba su hau kan mulkin ba.
“Tun a zaben da suka ce wai sun kayar da mu a Ekiti suka nuna cewa ko da karfin tsiya so suke su dawwama a kan mulki. Mu kuwa mu na da shaidar cewa ba a kayar da mu ba.” inji Fayose.
A karshe ya kara wa sanatocin kwarin-guiwar cewa su ci gaba da jajircewa, kada su bada kai bori ya hau.

Comments

Popular posts from this blog

Dadin kowa sabon salo episode 15

Dadin kowa sabon salo episode 15