Hadarin jirgin ruwa mai muni yaci mutane 17 yan kasuwa a jihar Kebbi


Jaridar Rariya ta dauko wnai rahoton hadarin jirgin ruwa mai muni daya faru a kauyen Garin Alhaji Ila cake cikin garin Yawurin jihar Kebbi, na jihar Kebbi. Wannan hatsari ya faru ne yayin da wani kwale kwale mai dauke da sama da mutane 50 ya kifa, bayan daya bigi wani katafaren ice, kamar yadda majiyar Hausazone.com ta ruwaito.
Dukan iccen keda wuya, sai jirgin ruwan ya dare gida biyu, hakan ya sanya jirgin nutsewa, inda mutane goma sha bakwai suka ce ga garinku nan, sa’annan mutane uku ba’a gansu ba sama ko kasa.

A nasa bangaren, shugaban karamar hukumar Yawuri, Musa Muhammad Yawuri ya bayyana alhininsa da faruwar wannan mummunan lamari, inda tare da kansilolinsa suka kai ziyarar ta’aziyya zuwa inda lamarin ya auku. A yayin ziyarar tasa, shugaban karamar hukumar ya bada umarnin a cigaba da neman sauran jama’a da ruwan yayi awon gaba dasu, sa’annan ya bada umarnina a garzaya da sauran gawawwakin zuwa babban Asibitin Yawuri.

Comments

Popular posts from this blog

BRIEF BIOGRAPHY OF SHEIKH IBRAHIM AHMAD MAQARY, IMAM OF NATIONAL MOSQUE ABUJA

Wane Ne Sheik Abul Fatahi Maiduguri? Karanta cikakken tarihin sa

TARIHI: ZUWAN TURAWA KASAR HAUSA DA YADDA SUKA CI KANO DA SOKOTO DA YAKI A SHEKARAR 1903.