AN JEFAR DA JARIRIYA DAUKE DA TAKARDAR WASIYYA A BIRNIN KEBBI



Daga Hamza Ahmed
Hukumar Hisbah ta jihar Kebbi ta gabatar da wata jaririya da aka haifa aka jefar a unguwar shiyar Sarakuna kusa da makarantar 'yan Mata mai suna Unity College a ranar Juma'a 22/12/17 da misalin karfe 11:00 na dare.
Yariyar an tsince ta ne cikin hijab, inda mahaifiyar yarinyar ta rubuta wasikar wasiya ta bari tare da jaririyar.
A cikin wasikar ta roka da don Allah a kula mata da diyarta ta, jefar da ita ne a dalilin tsangwamar da mahaifiyarta ta yi mata na a kashe jaririyar, shine ta zabi ta jefar da ita.
Ta kara da cewa tana rokon a sakawa jaririyar tata suna Aisha don shine sunan mahaifiyarta, ta kuma yi alkawarin cewa komai dadewa za ta waiwayo 'yartata.
Alh Abubakar Muhammad Lanne Augie, wanda shine Daraktan Shari'a a hukumar Hisbah, ya yi bayanin cewa wanna shine karo na farko da suka taba ganin irin wannan na a jefar da diya da wasiyya.
Ya yi bayanin cewa rokon da mahaifiyar yarinyar ta yi na a sawa diyar tata sunan mahaifiyarta, ya ce sun cika alkawarin, inda suka anso mata 'Court affidavit' dauke da sunan da ta roka a sawa diyar.
Daraktan ya kuma yi Allah wadai da yadda yawan jefar da yara ke karuwa.
A nasa bangaren, shugaban hukumar hisbah ta jihar, Alhaji Suleiman Muhammad ya yi kira ga musulmi su kara hada kai don sa ido a ga cewar an kawo karshen wannan lamarin. Ya roki Allah da ya shiryar da wannan matar ya kuma yi addu'a Allah ya raya wanna jariryar.
Domin karin bayani a tuntubi wanna lambar 07064343965

Comments

Popular posts from this blog

BRIEF BIOGRAPHY OF SHEIKH IBRAHIM AHMAD MAQARY, IMAM OF NATIONAL MOSQUE ABUJA

Wane Ne Sheik Abul Fatahi Maiduguri? Karanta cikakken tarihin sa

TARIHI: ZUWAN TURAWA KASAR HAUSA DA YADDA SUKA CI KANO DA SOKOTO DA YAKI A SHEKARAR 1903.